Monday, January 21, 2019

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN!!! KULLU NAFSIN ZA-IQATUL MAUT!!!


Aranar Asabar dindan ta gabata An yi wa ni babban rashi a garin Sheme, inda angon da aka daurawa aure tare da wasu daga cikin danginsa suka gamu da ajalinsu duka bayan kammala daurin aure.

An yi wani mummunan hadarin mota a ranar Asabar da tagabata a kan hanyar Sheme zuwa Funtua cikin karamar hukumar Faskari jihar Katsina, inda hadarin ya rutsa da angon da aka daurawa aure, da yayarsa mace da wansa da kuma wasu duk a kan hanyarsu ta zuwa Funtua bayan kammala daurin aurensa tare da na kanwarsa. Allah ya gafarta masu Ameen.

Mutane da dama a kafar sadarwar ta zamani musamman Facebook da WhatsApp na ta ci gaba da nuna alhininsu game da wannnan irin mutuwar fuju'a da ta afku ga wannnan amgon da a randa ake murnar saka shi dakin angunci, sai gashi zai tsinci kansa cikin dakin kewa na har abada.

Kwamrad Babangida Aliyu Sheme (Zamani) wanda shima dan uwa ne ga marigayen ya rubata cewa:

" Yan'uwan mu da Allah ya yi ma rasuwa jiya sanadiyar hadarin mota jiya Asabar akan hanyar su ta zuwa Funtua daga Sheme.

Wadanda suka rasu sun hada :

😭Hajiya Rakiya kanwar baban mamatan

😭Sadi Muhammad Angon da aka daurama auren jiya

😭Abubakar Muhammad kanin Angon

😭Wani danuwansu daga Funtua .

 Za a  yi jana'idarsu yanzu a garin Sheme .

Allah ya jikansu yasa Aljanna ce makoma a garesu, su kuma yan'uwa da abokanin arzuki Allah Ya bada hakurin jure Wannan Babban rashi. Ameen .

Abu Aiman Danja
Social Media Ta'aziyya.

No comments:

Post a Comment