Me Yasa 'Yan Social Media Basu Da Muhimmanci A Arewa?
Su Suka Jawowa Kansu!
1. Mecece Social Media?
Itace shafukan sadarwa na zamani wanda zasu baiwa mutum damar saduwa da wani ta hanyar rubutaccen sako, hoto, video, ko kira kai tsaye da akeyi. Social media sun hada da facebook, whatsApp instagram d.s.
2. Su Waye 'Yan Social Media?
Idan muka ka kalli ma'anar social media to masu amfani da wadannan shafukan sune 'yan social media, sai dai abin ba haka yake ba, idan akace 'yan social media sune wadanda suke Rubutu a shafukan internet, wadannan marubuta su ake kira a turance da Bloggers.
Yadda Abin Yake A Arewa:-
Daga sanda ka fara rubuta a social media mutane suna jin dadi to sai suyita zuga ka kai ga dan Social Media kullum kayi tayin abinda yake faranta musu koda kuwa abinda kake zai hanaka yin wajibinka na yin kwadagon kaiwa bakin salati.
Idan ka baiwa Mutane rayuwarka kana wannan aikin su kuma babu ruwansu da kana da bukata su dai kawai ka faranta musu duk randa ka gano kuskurenka ka juya zuwa ga fifita neman na halak dinka akan social media sai su fara aibata ka, wannan shine abinda yake faruwa a yanzu.
Abinda Yakamata Dan Social Media Yayi A Arewa:
Ya zama kana da sana'ar ka wadda itace kan gaba a Social Media ta yadda zaka iya rike kanka da ita.
Idan social media ta zame maka jiki kaje ka kashe kudi ka koyi yadda zaka dinga samun kudi ta harkar tunda halastacciyar sana'a ce.
Yaya Abin Yake A Kudu?
A kudu 'yan social media Mutane ne masu daraja a Idon al'umma amman sunyi daraja ne saboda suma sun daraja kansu a lokacin da dan Arewa ya shagala da shafin facebook kadai ka tara followers to sai aka kwace ko aka rufe maka account din Shikenan ka rasa shi?
Kowa ya san facebook na wani ne kaje kake haya kana biyan kudin Data don haka baka da cikakkiyar dama akai!
To su a kudu kowa yana kokarin samar da shafinsa wanda wannan shine darajar Marubuci a Social Media amman yau kaf marubutan APC na Arewa Bashir El-Bash kawai na san yana da shafi a Internet.
Ta Yaya Za'a Daraja ku?
Bari Kuji Ta Inda Bashir Ahmad Ya Faro:-
A shekarar 2010-2012 ina Junior Secondary ina shiga Google nayi research daga cikin bloggers na Arewa wanda nake gani shine Bashir Ahmad yana da wani blog na Wapka (tun ana yin Wapka), kunga kenan Bashir Ahmad Blogger ne kuma ya san komai na Blogging ya san mutum zai iya rike kansa ta blogging.
To don Allah daga wancan lokacin zuwa yanzu cikin 'yan APC kawai da mutum nawa ya dora a hanyar Blogging?
Yanzu kuna ganin inda ya dora su Biyora a hanyar domin suma su inganta rubutunsa ya zama yau in kana neman rubutun da Biyora yayi shekara kaza ka san inda zaka nemeshi kuma a internet ko ina rubutunsa zaije, yawan Followers da Biyora yake dashi da Bashir ya dorashi akai da yanzu Allah ne kadai ya san abinda zai dinga samu, kuma kuna ganin da zama a samu kofar da za'a nemi janyeshi?
1. Linda Ikeji ta fara blogging a 2006 yanzu a duniya idan akayi maganar Bloggers a Nigeria ita take zuwa ran kowa, yanzu shafinta har kamfanunuwa ke bata talla yau ta tsaya da kafarta kuma 'yar social media ce.
Ga sunayen wasu 'yan kudu duka matasa ne da abinda suka rika kenan yanzu sun wuce raini:-
2. Uche Eze Pedro ita tayi BellaNaija
3. Demola Ogundele shi yayi NotJustok
4. Kemi Filani tayi shafin Kemi Filani
5. Emeh Achenga ita tayi MespetitanNigeria
6. Ladun Liadi ita tayi shafin LadunLiadi
7. Noble Igwe me 360nobs
8. Japheth Omojuwa shi a yanzu yana cikin wadanda naganarsu ta zaga duniya dalilin hakan a ganinsu 'yan siyasa biyansa kudi suke don karma yayi magana akansu.
Wani zaice ni me yasa ban nuna musu ba?
Duk mai bibiyata yaga yanda nayi ta babatu akai kuma har mutane na nema duk mai sha'awar na koya masa kuma wanda suka ce suna bukata sun gani yanzu haka suna nan munayi wajen 100+ sun fara blogging 'yan arewa.
Allah ya kyauta.
Abu Aiman
Social Media Strategist.
No comments:
Post a Comment